A+ R A-
08 December 2023

Cikakken Jawabin Jagora Imam Khamenei Yayin Bikin Shekaru 31 Da Rasuwar Imam Khumaini (r.a)

Abin da ke biye fassarar jawabin da jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei yayi ne a ranar 3 ga watan Yunin 2020 don tunawa da shekaru 31 da rasuwar marigayi Imam Khumaini (r.a).

--------

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai

Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai. Tsira da amincin Allah su tabbata ga shugabanmu kuma Annabinmu Abul Ƙasim al-Mustafa Muhammad tare da Alayensa tsarkaka Ma'asumai musamman Wanzajjen Allah a bayan ƙasa.

A yau ana gabatar da bikin tunawa da marigayi Imam Khumaini da wani yanayi ba irin wanda aka saba gabatarwa ba. Yadda aka gudanar da biki ba shi ya ke da muhimmanci ba; asalin lamari kana kuma abu mai muhimmanci shi ne kalaman marigayi Imam waɗanda ƙasarmu take buƙararsu a yau da kuma a nan gaba. Shekaru bayan rasuwa ta zahiri da kuma rashinsa na zahiri, mu a wajen mu har yanzu Imam yana raye tare da mu kuma wajibi ne ya ci gaba da zama tare da mu, don kuwa lalle muna amfanuwa da kasantuwarsa da ruhinsa da tunaninsa da kuma shiryarwarsa.

A yau ɗin nan ina so ne in yi magana ne kan ɗaya daga cikin siffofi masu muhimmanci da Imaminmu mai girma ya keɓanta da su; duk kuwa da cewa shi ɗin nan wani mutum ne ma'abocin ɓangarori da kuma fitattun siffofi masu yawa da ya keɓanta da su. Waɗannan siffofin da a yau za mu yi magana kansu suna daga cikin siffofi mafiya muhimmanci da Imam ya keɓanta da su, su ne kuwa ruhin samar da sauyi da kuma son samar da sauyin da Imam yake da su. Imam a ruhance ya kasance mutum mai son sauyi kana kuma ma'abocin sauyi da samar da shi. Dangane da batun samar da sauyi, rawar da ya taka ba kawai rawa ce ta malami kana mai karantarwa kawai ba; (rawar da ya taka) wata rawa ce ta wani kwamandan yaƙi a yayin wani hari na soji kana kuma wani jagora da dukkanin ma'anar kalmar. A zamaninsa ya samar da mafi girman sauyi a fagage daban-daban masu yawan gaske, wanda a yau zan yi ishara da wasu daga cikinsu.

Da farko tsawon lokacin wannan ruhi na neman kawo sauyi ya kasance tare da wannan babban bawan Allah; ba wai wani abu ne da ya bayyana a tattare da shi a farko-farkon wannan yunƙuri na Musulunci a shekarar 1341 (1962) ba. A'a, shi ɗin nan tun lokacin samartakarsa ya kasance mutum ne mai son kawo sauyi, alamar hakan kuwa shi ne abin da ya rubutu tun yana saurayi – tun yana kimanin shekaru 30 – a littafin marigayi Waziri Yazdi, wanda marigayi Waziri ya taɓa nuna min wannan rubutun wanda Imam ya rubuta da hannunsa; na gani kuma daga baya ma an buga kuma da dama sun gani. A wannan rubutun, ya ambaci ayar nan ta «قُل إِنَّما أَعِظُکُم بِواحِدَةٍ أَن تَقوموا لِلَّهِ مَثنىٰ وَفُرادىٰ» (Ka ce: "Ina yi muku wa'azi ne kawai da kalma guda! Wato ku tsayu domin Allah, bibbiyu da ɗaiɗai) wacce take kiran mutane zuwa ga yunƙuri saboda Allah; ya kasance yana da irin wannan ruhin. Ya aiwatar da wannan ruhin a aikace, wanda kuma kamar yadda na faɗin ya haifar da sauyi. A aikace ya kasance a fagen sauyin ba wai kawai a magana da ba da umurni ba. Ya fara da samar da sauyi a tsakanin wasu gungun ɗaliban addini matasa a Ƙum – wanda a nan gaba zan yi ƙarin bayani kan hakan – har zuwa ga samar da gagarumin sauyi a tsakanin al'ummar Iran.

Wannan batu na Ƙum kuwa shi ne darasin Akhlaƙ (kyawawan halaye) da ya kasance yana karantarwa a can. Shekaru aru-aru kafin fara yunƙurinsa, baya ga darasin Fiƙihu da Usul, shekaru yayi yana karantar da Akhlaƙ a Ƙum. Koda ya ke mu a lokacin da muka je Ƙum, an daɗe da dakatar da waɗannan darussan, ba a yin su. Mutanen da suka shaidi waɗancan darussan suna faɗin cewa –sau ɗaya a kowane mako ya kasance yana ba da darasi a makarantar Fa'iziyya inda ɗalibai matasa su kan taru – yayin da yake magana, ya kan haifar da wani irin yanayi na sauyi a zukata. Mu ma da kanmu mun ga irin hakan a yayin darasinsa na Fiƙihu da Usul. Wato hatta a darussan Fiƙihu da Usul da yake bayarwa, a wasu lokuta ya kan yi magana kan kyawawan halaye, inda ɗalibai su kan fashe da kuka, lokacin da yake magana kan kyawawan halaye, ya kan zubar da hawaye. Haka maganganunsa su kan kasance masu tasiri da kuma haifar da sauyi da kuma ruhi na juyi. Wannan shi ne irin tafarkin Annabawa; Annabawa Allah a cikin dukkanin yunƙurinsu suna farawa ne da samar da sauyi na ruhi a tsakanin mutane. Abin da Amirul Muminina (a.s) yake faɗin na cewa: “Don su shiryar da su zuwa ga cika alƙawarin halittunSa, su sanar da su ni’imominSa…sannan su buɗe musu taskokin hikima da aka ɓoye” shi ne wannan. Wato “sannan su buɗe musu taskokin hikima da aka ɓoye” yana nufin suna farkar da waɗannan hikimomi da suke tattare da mutane da kuma shigar da su fagen motsi da yunƙuri da shiryar da dukkanin matakai da ayyukan mutane. Shi ma Imam da haka ya faro. Duk da cewa ni ba zan iya ikirarin cewa tabbas yana gudanar da waɗannan darussa ne don saboda daga baya hakan yayi sanadiyyar haifar da wani gagarumin yunƙuri na siyasa ba; lalle ni ban san hakan ba. To amma abin da babu kokwanto cikinsa shi ne cewa ƙoƙarin motsarwa da kuma yunƙurar da zukata wani tafarki ne da Imam ya riƙa yayin darasinsa na Akhlaƙ. Daga nan ne ya faro har ya haifar da gagarumin sauyi a fage mai faɗi na al'umma; shin a lokacin gwagwarmayar ne – wanda zan yi ishara da kuma kawo misalan hakan a nan gaba – ko kuma bayan nasarar juyin juya halin Musulunci, lalle ya haifar da gagarumin sauyi a cikin al'ummar Iran.

Ana iya ganin ci gaban jawabin ta nan:

Cikakken Jawabin Jagora Imam Khamenei Don Tunawa Da Shekaru 31 Da Rasuwar Imam

Labaran Da Suka Yi Kama Da Wannan

Ashura

Takaitaccen Bayani K...
Shafin Jagora Imam K...
Shafin Elwahabiya
Nemo Mu A Facebook